Lahadi 22 Maris 2026 - 09:41
Silsilar Tattaunawa Kan Mahdawiyya (12) | Rana a Bayan Giza-gizai 

Hauza / Batun Gaiba (boyuwar Imam) ba ya rushe hikimar da ke nuna wajabcin kasancewar Imam Ma‘sumi (a.s.); domin Imam yana nan a lokacin gaiba, kuma alfanunsa suna kaiwa ga mutane. Abin da kawai ba ya kaiwa ga mutane shi ne wani ɓangare na waɗannan alfanun saboda gazawar mutane da kansu a lokacin gaiba. Don haka mutane ne ya kamata su samar da shiri da cancanta domin samar da yanayin bayyanar (zuhur) na Imam.

Kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran  Hauza ya ruwaito, ana gabatar da jerin bahasoshi kan Mahdawiyya mai taken “Zuwa ga Al’umma Mai Manufa” domin yada koyarwa da ma’arifar da suka shafi Imam Mahdi (Allah ya gaggauta bayyanarsa) ga ku masu neman ilimi.

A cikin maganganun Imamai Ma‘sumai (AS) game da amfanin Imam da yake a boye, an kawo kyakkyawan misali inda aka kwatanta Imam Mahdi (AF) a lokacin gaiba da rana da take bayan gizagizai. Babu shakka wannan kwatanci yana da hikima mai zurfi. Saboda haka malaman Shi’a sun bayyana muhimman bayanai da dama game da wannan kwatanci, daga cikinsu akwai:

1. Rana ita ce cibiyar tsarin hasken rana. Haka ma Imam Zaman (AS) shi ne ginshiƙi da cibiyar rayuwar bil’adama.

2. Rana tana da fa’idodi da yawa a cikin halitta, kuma haskenta ɗaya ne daga cikinsu. Haka ma Imam Zaman (AS) yana da alfanu da yawa a tsarin halitta, kuma ƙanana kuma kaɗan daga cikinsu ne kawai suka dogara da bayyanar shi a fili.

3. Gizagizai suna rufe fuskar rana ga mutanen duniya, amma ba su sa duniya ta yi duhu gaba ɗaya ba. Haka ma Gaiba tana hana mutane ganawa da Imam kai tsaye, amma ba ta hana hasken alherinsa isa ga mutane ba.

4. Samuwar gizagizai daga tasirin duniya da mazaunanta ne, ba daga rana ba. Haka ma gaiba sakamakon ayyukan mutane ne.

5. Gizagizai suna hana hasken rana ne ga waɗanda suke ƙarƙashinsu. Idan mutum ya wuce su ya haura sama da su, ba za su hana shi hasken rana ba. Haka ma a lokacin Gaiba, idan mutum ya rinjayi sha’awoyin duniya kuma ya kai ga kamala, yana iya samun damar wuce shingen Gaiba ya samu haduwa da wannan rana da take ɓoye.

6. A amfana da rana ba ya bambanta tsakanin mai yarda da ita da mai ƙaryata ta. Haka ma alfanun halittar Imam suna isa ga kowa, ko mai imani da shi ko mai musunsa.

7. Wanda yake jiran gushewar gizagizai da gaske shi ne wanda ya fahimci muhimmancin rana sosai. Haka ma a lokacin Gaiba, sanin Imam sosai yana sa jira (intizar) ya zama na gaskiya.

Da sauransu.

Saboda haka babu shakka cewa amfanin da halittu ke samu daga rana yana ƙaruwa idan babu abin da ya rufe ta. Amma wannan ba yana nufin cewa idan akwai gizagizai to dukkan alfanun rana sun ɓace ba. A’a, wannan shinge yana rage wasu alfanun ne kawai.

Haka ma bayyanar Imam a zamanin zuhur yana nufin cewa dukkan alfanunsa na iya isa ga mutane. Idan wani abu ya hana cikakken alherinsa isa ga mutane, wannan ba yana nufin cewa wanzuwarsa ba ta da amfani ba. Wanzuwar Imam a bayan labulen gaiba tana da amfani kamar yadda wanzuwarsa ta kasance mai amfani a lokacin da yake cikin kurkukun sarakunan zalunci. Duk da cewa akwai bambance-bambance da yawa tsakanin kurkukun gaiba da kurkukun sarakunan zalunci, amma kowannensu a wani bangare yana hana cikakken alherin Imam isa ga halitta da mutane.

A takaice, batun gaiba ba ya soke hikimar wajibcin kasancewar Imam Ma‘asumi (AS); domin Imam yana nan a lokacin gaiba kuma alfanunsa suna isa ga mutane. Abin da kawai wasu daga cikin alfanun ba sa kaiwa shi ne saboda gazawar mutane da kansu. Saboda haka mutane ne ya kamata su shirya kansu su samar da yanayin da zai ba da damar bayyanar Imam.

Wannan bahasi zai ci gaba...

An ɗauko daga littafin “Farhangnameh‑ye Mahdawiyat” tare da ɗan gyara kaɗan.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha